Saurari premier Radio
34.9 C
Kano
Monday, May 20, 2024
Saurari Premier Radio
HomeLabaraiSiyasaAbinda Tinubu yaje yi a Turai | Premier Radio | 14.04.2023

Abinda Tinubu yaje yi a Turai | Premier Radio | 14.04.2023

Date:

APC ta ce shugaban kasa mai jiran gado Bola Ahmad Tinubu yana hutawa a Turai gabanin kama aiki gadan gadan bayan rantsuwa a 29 ga watan Mayu mai zuwa.

Sakataren yada labaran jam’iyyar na kasa, Felix Morka ne ya bayyana hakan a zantawarsa da kafar Channels.

Yace yanzu haka Tinubu na cikin koshin lafiya, kuma bayan sauke gajiyar zabe a Turai, zai dawo gida domin dorawa daga inda aka tsaya.

“Tabbas yanzu yana turai, cikin koshin lafiya. Ya yanke shawarar zuwa hutun ne bayan gamawa da hidimar zabe”, inji Morka.

“Da zararn ya dawo kuma ya karbi rantsuwa a 29 ga Mayu, babu sauran kakkautawa. Nauyin tafiyar da harkokin kasa irin Najeriya zai hau kansa. Na san yana gab da dawowa”.

Morka ya kara da cewa bai wai iya hutun ne kadai ya kai Tinubu waje ba, a’a, har da batun tattaunawa da shugabannin kasashen da ragowar masu ruwa da tsaki, domin tsara hanyoyin cimma manufofin gwamnatin sa cikin saukI.

Rashin jin duriyar shugaban mai jiran gado, ya haifar da cece kuce tsakanin jama’a musamman yan adawa, wadanda ke zargin Tinubun ya fita ne domin duba lafiyarsa, daya daga cikin abubuwan da ake ganin zasu hana shi mulki idan ya ci zabe.

Latest stories

Gwamnan Katsina ya nemi tallafi kan karancin abinci da matsalar tsaro ta haddasa.

A wani alk’amarin kuma, Gwamnan Katsina, Dikko Umaru Radda,...

Related stories

Atiku yace lokaci ya yi da za a yanke shawarar ko zai kara tsayawa takarar shugaban kasa

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar, yace magoya bayan...

Dan Ganduje ya kai wa Muhuyi ziyarar goyan bayan a binciki mahaifansa

Dan tsohon gwamnan Kano, Abdulaziz Abdullahi Ganduje, ya kai...