Mai rikon shugabancin kungiyar kwallon kafa ta Kano Pillars Dr. Ibrahim Galadima ya ce a wata mai zuwa, kungiyar za ta sanar da wanda zai jagoranci Pillars a sabuwar kakar wasannin shekarar 2022/2023.
Dr. Ibrahim Galadima ya ce shirye-shirye tuni sun kammala, domin sanar da sabon mai horar da kungiyar ta Sai Masu Gida domin fara shirin tinkarar kakar badi.
Dr. Galadima ya bayyana haka ne cikin wata sanarwa da mai Magana da yawun kungiyar Rulwan Idris Malika Garu ya aikewa Premier Radio da safiyar wannan rana.
Har ma ya bukaci magoya bayan kungiyar, dama masu ruwa da tsaki da su ci gaba da hakuri da kuma yiwa kungiyar fatan nasara a sabuwar kakar wasanni mai kamawa.