Saurari premier Radio
41.1 C
Kano
Monday, April 29, 2024
Saurari Premier Radio
HomeFIFAAbin da ya kamata ku sani kan Yunkurin Fara Amfani da Shudin...

Abin da ya kamata ku sani kan Yunkurin Fara Amfani da Shudin – Kati a kwallon Kafa

Date:

Hukumar da ke Kula da tsara dokokin kwallon kafa ta duniya IFAB ta ce, za ta tattaunawa batun fara amfani da shuɗin-kati (Blue Card) a wasannin Kwallon kafa.

Ana sanar hukumar ta IFAB za ta gudanar da babban taron ta na Shekara-shekara a cikin watan Maris mai zuwa a kasar Scotland.

Inda ake saran hukumar za ta Tattaunawa batun fara amfani da Shudin-Kati a yunkurin fara amfani da shi a wasannin League na kasashe.

Da zarar amfara amfani da Shudin-Katin, dan wasa zai kwashe minti 10 a wajen fili yana hutawa idan Alkalin wasa ya ba shi shuɗin katin.

A yanzu dai ana amfani ne da katuna biyu, wato kati mai ruwan ɗorawa (Yellow card) a matsayin katin gargaɗi, da kuma jan kati (Red card) a matsayin katin kora da zarar mutum ya yi keta mai girma.

Dama dai ana amfani da shudin kati a wasannin kwallon kafa a mataki na kasa-kasa, sai dai ana sa ran kawo shi cikin manyan gasannin League domin fara amfani da shi.

To amma babu tabbacin ko yaushe za a fara gwajin shudin katin da kuma gasar da za a fara yin gwajin musamman a wasannin nahiyar turai.

Yanzu haka tuni gasar Firimiya ta Ingila ta kushe batun gwajin katin a wasanninta, yayin da hukumar kwallon kafa ta duniya FIFA ta ce bai kamata a fara batun amfani da katin a manyan gasannin duniya ba a yanzu.

Dama wasu na ganin matakin kasar Ingila na kawar da batun ba abin mamaki bane, domin ko a Lokacin fara amfani da na’urar VAR kasar da fari ta kushe batun kafin daga bisani tayi mi’ara koma baya.

Latest stories

Ƙungiyar Hamas ta isa birnin Al-Qahira game da tattaunawa kan tsagaita wuta.

Rahotanni daga kasar Masar, sun ce tawagar jami’an kungiyar...

An kashe ƴan ƙato da gora sama da 23 a Barno da Sakkwato.

Rahotanni daga jihohin Borno da Sakkwato sun ce, an...

Related stories

NPFL: Gwamnatin Kano ta bawa Kano Pillars wasa Uku domin ta yi Nasara

Gwamnatin Jihar Kano ta bawa kungiyar Kwallon kafa ta...

AFCON 2023: Kashim Shettima ya tafi Cote d’Ivoire don marawa Super Eagles baya

Mataimakin shugaban kasa Kashim Shettima, ya bar Najeriya zuwa...