Kungiyar kwallon kafa ta Manchester City ta fice daga gasar cin kofin Carabao Cup, bayan rashin nasara a hannun Southampton da ci 2-0.
Wasan dai ya gudana a ranar Laraba a filin wasa na St. Mary’s da ke Ingila.
Yan wasan kungiyar kwallon kafa ta Southampton’s Sekou Mara da Moussa Djenepo ne suka zura kwallaye biyun a minti na 23rd da 28.
Yanzu haka dai kungiyar kwallon kafa ta Southampton ta kai wasan kusa da karshe a gasar ta Carabao Cup.
Inda Southampton zata kece raini da Newcastle, sai kuma Nottingham Forest da Manchester United.
Wasannin kusa da karshen za gayen farko zasu gudana A ranar 23 ga Janairun da muke ciki.
Sai kuma wasannin za gaye na biyu na gasar ta Carabao Cup za su gudana a ranar 30 ga watan na Janairun..
Haka kuma wasan karshe zai gudana a katafaren filin wasa na Wembley a ranar Lahadi wato 26 ga Fabrairu Mai kamawa .