By Faisal Abdullahi Bila
Gwamnatin tarayya ta ce zata kara harajin kashi talatin kan taba sigari a matasyin wani bangare na rage shan ta a kasar.
Shugaba sashen kula da cutuka marasa yaduwa a ma’aikatar lafiya ta rayya Dr Mangai Malau ne ya bayyana hakan a ranar talata yayin taron wayar da kai kan rage ta’ammali da taba sigari na kasa a Abuja.
Malau yace gwamnatin tarayya ta kara harajin ne daga kashi 30 zuwa 50 saboda ya zo dai dai da tsarin hukumar lafiya ta duniya.
Ya kara da cewa hakan zai taimakawa wajen rage shan taba, don haka akwai bukatar masu ruwa da tsaki su yi amfani da sanya harajin ta hanyar da ta dace don ganin an magance matsalar yawan shanta a kasa baki daya.