Gwamnatin tarayya ta bada izinin sake daukar ma’aikatan da suka yi ritaya a fannin lafiya domin sake farfado da fannin.
Wannan ya biyo bayan hijira da likitocin kasar nan da sauran jamian lafiya ke yi zuwa kasashen waje domin samun gwaggwaban albashi da yanayi mai kyau.
Umarnin sahalewar na kunshe cikin wata sanarwa da aka rabawa manyan jamian hukumar masu kula da cibiyoyin lafiya a kasar nan, ranar 5 ga watan oktobar nan.
Wadanda aka sahale a dauka sun hada da likitoci da jamian jinya. Takardar da babban sakatare mai kula da manufofi da tsare-tsare a hukumar ya sanyawa hannu ya bayyana cewa ma’aikatan sun yi watsi da yunkurin gwamnati na kara yawan shekarun ritaya ga ma’aikatan lafiya daga shekara 65 zuwa 70.