A wannan rana ta Litinin 7 ga Nuwambar 2022 aka gudanar da rabon bikin jadawalin zagaye na kungiyoyi 16 a gasar cin kofin zakarun turai Champion League.
Rabon jadawalin ya gudana a wannan rana ta Litinin a birnin Nyon na kasar Switzerland.
Inda kungiyo daban-daban zasu fafata tsakaninsu.
RB Leipzig zata kece raini da Manchester City
Club Brugge da Benfica
Liverpool da Real Madrid
AC Milan da Tottenham
Eintracht Frankfurt da Napoli
Borrusia Dortmund da Chelsea
Bayern Munich da PSG
Inter Milan da FC Porto
Ana saran wasannin zasu ci gaba da gudana bayan kammala gasar cin kofin duniya da zata gudana a kasar Qatar a karshen Shekarar da muke ciki.