Hukumar gudanarwar kungiyar kwallon kafa ta Kano Pillars ta dakatar da mai horas da yan wasanta, Abdu Maikaba nan take.
Hakan ya biyo bayan kafa wani kwamiti da zai binciki aikin kocin tare da bayar da shawarar daukar mataki na gaba.
Idan dai za a iya tunawa, Abdu Maikaba yayi wasu kalamai na rashin jin dadi dadi a kwanakin baya game da gudanarwar kungiyar yayin wani taro da magoya bayan Kano Pillars din suka shirya a nan Kano.
Matakin dakatar da shi ya zo ne kwanaki bayan da tsohon dan wasan Enugu Rangers din ya bayyana cewa bai samu ingantaccen yanayin aiki ba tun lokacin da ya karbi ragamar shugabanci a farkon kakar bana.