Saurari premier Radio
31.9 C
Kano
Sunday, May 19, 2024
Saurari Premier Radio
HomeLabaraiDa Dumi-dumiBinance na zargin jami'an Najeriya da neman cin hancin dala miliyan 150.

Binance na zargin jami’an Najeriya da neman cin hancin dala miliyan 150.

Date:

Kamfanin Binance ya zargi wasu manyan jami’an gwamnatin Najeriya da neman cin hancin dala miliyan 150 a kuɗin kirifto domin a kawo ƙarshen tuhumar da ake masa.

Shugaban kamfanin, Richard Teng ne ya bayyana haka a wani shafin intanet, kamar yadda jaridar New York Times ta wallafa.

A cewar rahoton na jaridar ta New York Times, Tigran Gambaryan, jami’i a a kamfanin, ya yi iƙirarin cewa ya samu wani saƙo mai ɗaga hankali a wata tafiya da ya yi zuwa Najeriya a watan Janairu.

Rahoton ya ce “a wata ziyara zuwa Najeriya a watan Janairu, Tigran Gambaryan, jami’i a kamfanin Binance mai hada-hadar kirifto, ya samu wani saƙo mai tayar da hankali. An bai wa kamfanin kwana huɗu su biya dala miliyan 150 a kuɗin kirifto,”

Gambaryan, wanda tsohon jami’in tsaro ne a Amurka, ya fahimci saƙon a matsayin neman na goro daga wani a gwamnatin Najeriya, a cewar wasu mutum biyar da suka san da batun da kuma nazarin saƙon da jaridar New York Times ta yi.

Shi da abokan aikinsa na Binance sun gana da ƴan majalisar dokokin Najeriya da suka zargi kamfanin da kauce wa biyan haraji da kuma barazanar kama ma’aikatan kamfanin.”

Bayanai sun nuna cewa lamarin ya faru ne kafin a kama Gambaryan da abokin aikinsa Nadeem Anjarwalla bisa umarnin mai bai wa shugaban kasa shawara kan sha’anin tsaro, Nuhu Ribadu.

Daga bisani kuma Anjarwalla ya tsere inda aka gano shi a Kenya.

A martaninsa, kakakin ofishin Ribadu, Zakari Mijinyawa ya bai wa gwamnati tabbacin bin ƙa’ida.

Mijinyawa a cewar wani saƙo da aka aike wa jaridar New York Times, gwamnati za ta bayyana hujjojinta, bisa tsarin doka.

BBC HAUSA

Latest stories

Atiku yace lokaci ya yi da za a yanke shawarar ko zai kara tsayawa takarar shugaban kasa

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar, yace magoya bayan...

Related stories

Atiku yace lokaci ya yi da za a yanke shawarar ko zai kara tsayawa takarar shugaban kasa

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar, yace magoya bayan...