Shirye shirye sun kammala na ziyarar shugaba Buhari garin Maiduguri a gobe Alhamis.
Wannan dai itace ziyarar aiki karo na uku cikin shekara daya bayan wacce ya kai jihar ranar 17 ga watan Yuni da 23 ga watan Disambar shekarar 2021.
Buhari ya nada Dangote shugaban kwamitin dakile cutar malaria na kasa.
Yayin ziyarar anasa ran shugaba Buhari zai bude ayyukan tallafawa wadanda matsalar tsaro ta shafa da bude rukunin gidajen malaman makaranta a Bukumkutu da wasu gidaje 500 a Molai wadanda gwamnatin jihar ta samar.
A na kuma sa ran zai ziyarci shehun Borno yayin ziyarar.
Ana kuma shawartar masu ababen hawa sa su fita da wuri don kaucewa cin koson ababen hawa.