Saurari premier Radio
23.8 C
Kano
Saturday, July 27, 2024
Saurari Premier Radio
HomeLabaraiKiwon LafiyaBuhari ya nada Dangote shugaban kwamitin dakile cutar malaria na kasa.

Buhari ya nada Dangote shugaban kwamitin dakile cutar malaria na kasa.

Date:

Karibullah Abdulhamid Namadobi

 

Shugaba Muhammadu Buhari ya nada  Alhaji Aliko Dangote a matsayin shugaban kwamitin dakile cutar zazzabin cizon sauro na kasa wato malaria.

 

Rahotanni na cewar Buhari ya nada Dangote ne saboda gudummuwar da yake bayarwa a bangaren lafiya a nahiyar Afirka bakidaya.

 

Shugaban kasa Muhammadu Buhari ya bayyana haka ne yayin kaddamar da kwamitin mai mutane 16 a ranar Talata, inda ya ce nasararsu a aiwatar da shirin za ta taimaka wajen rage kudin da cutar ke lakumewa daga tattalin arzikin kasa.

 

Kudin da aka kashewa kan cutar malaria ya kai Naira milyan dubu 687 a bana.

 

Shugaban ya kuma sanar da kwamitin cewa baya ga inganta lafiya, shirin zai amfani zamantakewa da tattalin arzikin kasar nan.

Latest stories

246943801721751646

246943801721751646

SANARWAR JANYEWA DAGA TAKARA DAGA SHUGABA JOE BIDEN NA AMURKA.

SANARWAR JANYEWA DAGA TAKARA DAGA SHUGABA JOE BIDEN NA...

Related stories

246943801721751646

246943801721751646

SANARWAR JANYEWA DAGA TAKARA DAGA SHUGABA JOE BIDEN NA AMURKA.

SANARWAR JANYEWA DAGA TAKARA DAGA SHUGABA JOE BIDEN NA...