Karibullah Abdulhamid Namadobi
Shugaba Muhammadu Buhari ya nada Alhaji Aliko Dangote a matsayin shugaban kwamitin dakile cutar zazzabin cizon sauro na kasa wato malaria.
Rahotanni na cewar Buhari ya nada Dangote ne saboda gudummuwar da yake bayarwa a bangaren lafiya a nahiyar Afirka bakidaya.
Shugaban kasa Muhammadu Buhari ya bayyana haka ne yayin kaddamar da kwamitin mai mutane 16 a ranar Talata, inda ya ce nasararsu a aiwatar da shirin za ta taimaka wajen rage kudin da cutar ke lakumewa daga tattalin arzikin kasa.
Kudin da aka kashewa kan cutar malaria ya kai Naira milyan dubu 687 a bana.
Shugaban ya kuma sanar da kwamitin cewa baya ga inganta lafiya, shirin zai amfani zamantakewa da tattalin arzikin kasar nan.