Watanni 8 bayan kai hari ga gidan yarin kuje dake Abuja, rahotanni na cewa har kawo yanzu akwai fursunoni 460 da suka tsere ba tare da an kamasu ba.
Jaridar the punch ta gano bayanan fursunonin a ranar juma’a ta hannun hukumar kula da gidajen yari ta kasa.
Idan za’a Iya tunawa dai an kai harin gidan yarin na Kuje a ranar 5 ga watan yulin a shekarar 2022, abinda yayi sanadiyyar tserewar fursunoni da dama cikinsu har da yan ta’addar boko haram 64.
Tuni dai rahotanni suka bayyana cewar an samu damar sake kama mutane 421 da suka tsere, Inda aka watsa bayanan sauran fursunonin da ba’a samu nasarar kamawa ba ga yan sandan dake kula da yan ta’adda na duniya.