Gwamnan Kano mai jiran gado Abba Kabir Yusuf ya kaddamar da kwamitin karbar mulki a ranar 29 ga watan Mayu na 2023 dake tafe.
A wani taro da aka kammala a yammacin yau, Abba Kabir Yusuf ya kaddamar da kwamitin mutum 65 karkashin jagorancin Abdullahi Baffa Bichi a matsayin shugaba da kuma Abdullahi Musa a matsayin sakatare.
Wannan na zuwane bayan da hukumar zabe INEC ta damkawa zababben gwamnan na Kano shaidar lashe zaben gwamnan jihar nan.
Kwamitin da Abba Kabir Yusuf ya kaddamar a yau zaiyi aiki tun daga yau har zuwa lokacin da za’a rantsar da zababben gwamnan na Kano karkashin jamiyyarshi ta NNPP.