Gwamnan Kano Abba Kabir Yusuf ya bada umarnin rushe duk wasu gine-gine da akayi ba bisa ka’ida ba.
Gine-ginen sun hada da wanda akayi a masallatai, makarantu, makabartu, asibitoci, kasuwanni, filayan wasa da sauransu.
A cikin wata takadda mai dauke da sa hannun sakataran yada labaran gwamna Sunusi Bature Dawakin-Tofa yace daman gwamnan Kano Abba Kabir Yusuf yayi alkawarin daukar wannan mataki a yayin da yake yakin neman zabe.