Saurari premier Radio
29.9 C
Kano
Tuesday, May 21, 2024
Saurari Premier Radio
HomeLabaraiDokar takaita cire kudi da CBN ya sanya ta fara aiki a...

Dokar takaita cire kudi da CBN ya sanya ta fara aiki a yau litinin

Date:

Karibullah Abdulhamid Namdobi

 

Sabuwar dakar babban bankin kasa CBN ya sanya ta takaice cire kudi a kasar nan ta fara aiki yau litinin 9 ga watan janairun 2023.

 

CBN dai ya sanya dokar takaita cire kudi a rana guda, inda mutum daya ke da damar cire naira dubu 500 yayin da kamfanoni suke da damar cire miliyan 5.

 

Baya ga haka bankin na CBN ya umarci bankuna a kasar nan su daina sanya tsaffin kudi a na’urar ATM.

 

Umarnin dai na zuwane yayin da a karshen watan Janairu za a daina amfani da tsaffin kudi na naira 1000 da 500 da 200 a fadin Najeriya.

 

Sabbin dokokin da CBN ya sanya wasu na ganin zasu taimaka wurin takaita zagayawar kudi barkatai tsakanin alumma a kasar nan.

 

A gefe guda kuma dokokin sun janyo cece-kuce, abinda har yanzu wasu ke kokawa kan irin yadda lamarin ka iya janyowa wasu yan kasar nan asara.

Latest stories

Gwamnan Katsina ya nemi tallafi kan karancin abinci da matsalar tsaro ta haddasa.

A wani alk’amarin kuma, Gwamnan Katsina, Dikko Umaru Radda,...

Related stories

Gwamnan Katsina ya nemi tallafi kan karancin abinci da matsalar tsaro ta haddasa.

A wani alk’amarin kuma, Gwamnan Katsina, Dikko Umaru Radda,...