Saurari premier Radio
31.9 C
Kano
Monday, May 6, 2024
Saurari Premier Radio
HomeLabaraiGwamnatin KanoGwamnatin Kano Ta Yiwa Masu Zubar Da Shara A Hanya Allah Ya...

Gwamnatin Kano Ta Yiwa Masu Zubar Da Shara A Hanya Allah Ya Isa.

Date:

Daga Muktar Yahya Usman

Gwamnatin Kano ta yiwa masu zubar da shara akan hanyoyi da titunan jihar Allah ya Isa.

 

Kwamishinan Muhalli Dr Ibrahim Getso ne yayi Allah ya isar yayin duban tsaftar Muhalli na karshen wata.

 

Getso ya ce abin takaici ne yadda jama’a suka mayar da hanyoyi wurin zuba shara.

 

Ya ce ko kadan gwamnati ba za ta lamunci cin kashin da jama’a ke yi a hanyoyin Kano ba.

 

” Gwamnati ita kadai ba za ta iya ba, akwai bukatar jama’a da kungiyoyi su shigo cikin wannan aiki,Mu hada kai domin a samu nasarar tsaftace muhallinmu, domin mu muke zaune a cikinsa.” A cewar Kwamishinan.

Latest stories

Sarkin musulmi ya ja hankalin shugabanni kan samarwa da al’umma makoma

Mai alfarma sarkin musulmi Alhaji Sa’ad Abubakar na 3...

Related stories

Sarkin musulmi ya ja hankalin shugabanni kan samarwa da al’umma makoma

Mai alfarma sarkin musulmi Alhaji Sa’ad Abubakar na 3...