Saurari premier Radio
29.9 C
Kano
Saturday, May 4, 2024
Saurari Premier Radio
HomeLabaraiKADUNA: Sanata Shehu Sani ya nemi a hadashi muhawara da dan takarar...

KADUNA: Sanata Shehu Sani ya nemi a hadashi muhawara da dan takarar gwamna a jam’iyar APC

Date:

Sanata Shehu Sani, ya nemi a hadashi muhawara da wanda jam’iyar APC zata tsayar amatsayin dan takarar gwamna a jihar Kaduna.

‘Yan majalisar dokokin Kano 10 sun sauya sheka daga PDP zuwa NNPP

Tsohon sanatan Kaduna ta tsakiya kuma dan takarar gwamna a jam’iyar PDP Sanata Shehu Sani, ya ce ya kosa a hadashi yin muhawara a bainar al’umma tare da duk wani dan jam’iyar APC da za a baiwa tikitin tsayawa takarar gwamna a jihar.

Sanata shehu sani ya bayyana hakane a shafin san a Facebook a Litinin din nan.

Ya ce akwai maganganu a bakin sa masu zafi da daci kuma jama’a zasu so suji su.

“Wallahi na kosa muyi muqabala a bainan jama’a da Duk dan APC da za’a baiwa ticket na Kaduna;Akwai maganganu masu zafi da dachi daki daki da make jiransu dashi. Jama’a zasu ji abun da basu taba ji ba. Babban rufin asirin su,Idan bani Allah ya baiwa ba,” a cewar Sanata Shehu Sani.


Sanata Shehu Sani, dai ya sayi fom na tsayawa takarar gwamnan jihar Kaduna karkashin jam’iyar adawa ta PDP a zabe mai zuwa na shekarar 2023.

 

A kwanakin bayane dai gwamnan Kaduna Nasir El-Rufa’I ya bayyana Sanata Uba Sani a matsayin wanda zayyi takarar gwamna a jam’iyar APC a jihar Kaduna.

Latest stories

2023 ita ce shekara mafi muni ga yan jarida.

Hukumar Kare Haƙƙin Ɗan'adam ta Majalisar Ɗinkin Duniya ta...

Muna duba batun mafi karancin albashi-Gwamnoni.

Kungiyar gwamnonin kasar nan, ta ce kawo yanzu tuni...

Related stories

2023 ita ce shekara mafi muni ga yan jarida.

Hukumar Kare Haƙƙin Ɗan'adam ta Majalisar Ɗinkin Duniya ta...

Muna duba batun mafi karancin albashi-Gwamnoni.

Kungiyar gwamnonin kasar nan, ta ce kawo yanzu tuni...