Saurari premier Radio
30.9 C
Kano
Sunday, May 19, 2024
Saurari Premier Radio
HomeLabaraiRashin ilimi ne yasa matasa ke aikata ta'addanci a Kano: Dan majalisar...

Rashin ilimi ne yasa matasa ke aikata ta’addanci a Kano: Dan majalisar jiha mai wakiltar Bebeji Ali Muhd Tiga

Date:

Rashin ilimi ne yasa matasa ke aikata ta’addanci a Kano: Dan majalisar jiha mai wakiltar Bebeji Ali Muhd TigaDan majalisar jiha mai wakiltar Bebeji, Ali Muhammad Tiga, ya bayyana damuwar sa kan halin da ilimi ya tsinci kansa a jihar Kano.

Ali Muhd Tiga, na wannan jawabi ne yayin taron bada horo ga ‘yan majalisar dokokin Kano na majalisa ta goma.

Ya ce kasancewar sa matashi yana takaicin yadda matasa da yawa basa samun damar zuwa makaranta wanda hakan ke kara ta’azzara matsalolin rashin tsaro a jihar Kano.

Kwanaki hudu na mulkin gwamna Abba Kabir Yusuf yafi shekaru takwas na mulkin Ganduje: Shugaban jam’iyar NNPP

Ya kara da cewa zai maida hankali wajen kawo kudororin da zasu magance matsalolin shaye shaye da wadanda zasu raya karkara.

Ali Muhammad Tiga, ya ce zai maida hankali wajen samarwa da matasan yankin Bebeji aikin yi da bada jari da samar da sana’o’in dogaro dakai.

Ya nuna farin cikin sa bisa yadda aka basu horon sanin makamar aiki kasancewar su sabbin mambobi a majalisa.

Latest stories

Atiku yace lokaci ya yi da za a yanke shawarar ko zai kara tsayawa takarar shugaban kasa

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar, yace magoya bayan...

Related stories

Atiku yace lokaci ya yi da za a yanke shawarar ko zai kara tsayawa takarar shugaban kasa

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar, yace magoya bayan...