Saurari premier Radio
28.9 C
Kano
Friday, May 17, 2024
Saurari Premier Radio
HomeLabaraiDa Dumi-dumiMinistan harkokin wajen Masar ya gana da na Faransa dangane da yadda...

Ministan harkokin wajen Masar ya gana da na Faransa dangane da yadda za a tsagaita wuta a zirin Gaza.

Date:

A halin da ake ciki kuma, rahotanni sun tabbatar da cewa, ministan harkokin wajen Masar, Sameh Shoukry, ya gana da takwaransa na Faransa dangane da yadda za a tsagaita wuta a Zirin Gaza domin kawo karshen zubar da jinin Falasdinu da Isra’ila ke yi.

Ziyarar da ministan harkokin wajen Faransa Stephane Sejourne ya kai birnin Alkahira, ta zo ne bayan ganawar wakilan Amurka da Masar da Qatar a farkon wannan mako, inda Isra’ila ta gabatrwa kungiyar Hamas tayin kulla yarjejeniyar tsagaita wuta ta kwana arba’in.

Har zuwa lokacin hada wannan rahoto mayakan Hamas na nazari kan wannan tayi da ya kunshi musayar fursunoni tsakaninsu da Isra’ila, kusan wata bakwai bayan barkewar yaki a Zirin Gaza.

Shugaban Hamas, Suhail al-Hindi, ya shaidawa manema labarsai cewa, nan ba da jimawa ba zasu bayyana matsayarsu game da wannan batu.

Haka-zalika, Isra’ila ta ce ta na kan tattaunawa, tare da jiran amsar kungiyar Hamas.

 AAG

Latest stories

Kananan Hukumomi 14 A Kano Na Fuskantar Barazanar Ambaliya A Bana

Mukhtar Yahya Usman Hukumar kula da yanayı ta kasa NİMET...

Related stories

Kananan Hukumomi 14 A Kano Na Fuskantar Barazanar Ambaliya A Bana

Mukhtar Yahya Usman Hukumar kula da yanayı ta kasa NİMET...