Manoman kubewa a fadin kasar nan sun koka game da wata sabuwar cuta da ke addabar gonakinsu.
Manoman sun bayyana yadda cutar ta lalata kusan kashi saba’in cikin dari na kayan amfanin gonakinsu.
Cibiyar binciken kayan lambu ta kasa ta tabbatar da gano kwayar cutar yayin tattara rahotannin da ta samu daga manoman kasar nan daban-daban, musamman a jihohin Lagos, da Osun, da Ondo, da Oyo, da Ogun, da Neja, da jihar Ekiti.
Hukumar ta ce alamun cutar sun hada da wani kullutu da ke fitowa a karkashin ganyen kubewar, inda daga bisani yake nannadewa tare da sauya launi zuwa rawaya.
Cibiyar binciken kayan lambun ta shawarci manoman su yi wa gonakin kubewarsu feshin maganin kwari kowanne mako da zarar sun ga alamun cutar, tare da bayar da tabbacin dukufa wajen bincike domin samar da nagartaccen maganin da zai kashe cutar nan ta ke.