Kungiyoyin kwadago na kasa NLC da TUC zasu tsunduma yajin aikin bai daya a fadin kasar nan ranar Talata 14 ga watan Nuwamba 2023.
Shugabannin kungiyoyin biyu sun cimma wannan matsaya ne bayan wani taron majalisar zartarwa ta kasa na musamman da aka gudanar a ranar Talatar nan a Abuja.
Matakin da kungiyar kwadagon ta dauka ya biyo bayan cin zarafin shugaban NLC na kasa, Joe Ajaero, a makon jiya a jihar Imo.
Tun a safiyar gobe laraba yan kwadago a jihar Imo zasu tsunduma yajin aiki kafin sauran yan kungiyar su biyo baya.
Kungiyar kwadagon de na zargin kwamishinan ‘yan sanda na jihar Imo, Mohammed Barde da hannu a harin da aka kaiwa Ajaero a Owerri, babban birnin jihar Imo.