Saurari premier Radio
39.9 C
Kano
Thursday, May 16, 2024
Saurari Premier Radio
HomeLabaraiDa Dumi-dumiKawo Yanzu Gwamnatin Kano Ta Gaza Cika Alkawarin Karin Naira Dubu 20...

Kawo Yanzu Gwamnatin Kano Ta Gaza Cika Alkawarin Karin Naira Dubu 20 Da Ta Yiwa Ma’aikata

Date:

Kungiyar kwadago ta TUC reshen jihar Kano, ta ce za ta binciki dalilin rashin biyan ma’aikata dubu 20-20 da gwamnatin jihar ta yi alkawarin farawa daga watan Disambar bara.

A shekarar da ta gabata ne gwamna Abba Kabir Yusuf, ya yi alkawarin yiwa ma’aikatan kananan hukumomi da na jiha karin dubu 20n-20n a albashinsu na tsawon wata shida, wanda zai fara daga watan Disambar 2023, da nufin rage musu radadin rayuwa.

Sai dai rahotanni sun bayyana cewa tuni aka fara biyan albashin watan Janairu ba tare da karin dubu 20-20 din ba.

Shugaban kungiyar kwadagon ta TUC reshen Kano, kwamred Mubarak Buba Yarima, ya shaidawa wakiliyarmu, Hauwa Halliru Gwangwazo, cewa za su tuntubi gwamnatin Kano kan wannan batu, sai dai ya ce ma’aikatan su sani cewa kudin zai zo ne daban ba wai a cikin albashinsu ba.

Gwamnatin Kano dai ta yi alkawarin inganta rayuwar ma’aikatan jihar domin samun ci gaba.

Latest stories

Kananan Hukumomi 14 A Kano Na Fuskantar Barazanar Ambaliya A Bana

Mukhtar Yahya Usman Hukumar kula da yanayı ta kasa NİMET...

Related stories

Kananan Hukumomi 14 A Kano Na Fuskantar Barazanar Ambaliya A Bana

Mukhtar Yahya Usman Hukumar kula da yanayı ta kasa NİMET...