Sheikh Daurawa ya sauka daga mukaminsa na babban kwamandan Hisbah
Daurawa ya bayyana hakan a wani fefen bediyo daya daura a shafinsa na Facebook a safiyar yau.
Wannan na zuwa kasa da awanni 24 da jawabin gwamnan Kano da ya nuna rashin Jin dadinsa bisa yanda hukumar Hisbah take tafiyar da kamen wadanda ake zargi da aikata laifi.
Malamin yace yayi iya kokarinsa wajen gyaran tarbiyar matasan Kano musamman Yan Tiktok da Yan film amman abu yaci tura.
Ya nemi afuwar Gwamnan Kano bisa yanda ya sauka daga mukaminsa bakatatan.