Jam’iyyar APC mai mulki a jihar Kano ta bai wa hukumar zabe mai zaman kanta ta Najeriya INEC mako daya ta sake nazari kan sakamakon zaben gwamna na jihar da aka yi ranar 18 ga watan Maris.
jam’iyyar APC Kano ta ce bata yarda da sakamakon zaben gwamnan Kano da ya bayyana Abba Kabir na jam’iyyar NNPP a matsayin wanda ya lashe shi ba.
jam’iyyar ta bayyana haka ne ta bakin lauyantaBarista Abdul Fagge a taron manema labaran da ta gudanar ranar Talata.
APC ta ce baturen zaben ya yi kuskuren fahimtar dokar zabe wajen banbance soke sakamakon wasu wurare da aka yi sanadin tashin hankali da kuma zabe fiye da kima.
APC dai ta ce sam ba ta yadda da hanyar da aka bi wajen sanar da sakamakon zaben ba har aka bayyana Abba Kabir a matsayin zababben gwamna a don haka ta nemi a gaggauta sake yin zagaye na biyu na zaben.
Sai dai a cewar lauyan, baturen zaben ya yi la’akari ne kawai da batun tashin hankali wajen kare tazarar da ke tsakanin yan takara biyu – Abba Kabir Yusuf na NNPP da Nasir Gawuna na APC