Hukumar bayar da agajin gaggawa ta jihar Kano ta ce tana cigaba da tattara alkaluma na shagunan da iftila’in gobara ya rutsa dasu a kasuwar Kurmi dake nan Kano.
Shugaban hukumar na Kano Dr Sale Jili ne ya bayyana haka a zantawarsa da Premier radio da safiyar Asabar din nan.
Ya kara da cewa kimanin sama da naira miliyan 140 akayi asara a gobarar hakan yasa suke tattara bayanai domin samarwa yan kasuwar tallafin daya dace.
A lahadin data gabata ne gobarar ta tashi a wannan kasuwa da tayi sanadiyyar konewar sama da shaguna 80 da asarar dumbin dukiyoyi.