Saurari premier Radio
41.9 C
Kano
Friday, May 3, 2024
Saurari Premier Radio
HomeLabaraiGwamnonin Najeriya zasu gudanar da taro kan tattalin arziki.

Gwamnonin Najeriya zasu gudanar da taro kan tattalin arziki.

Date:

Mukhtar Yahya Usman

 

Gwamnonin jihohi kasar nan 36 za su gidanar da wani muhimmn taro a ranar Laraba a Abuja domin tattauna batutuwan da suka shafi tattalin arziki da matsalolin tsaro da sauran kalubalen da ke addabar al’ummar kasar.

 

Daraktan yada labaran gwamnonin kasar nan Abdulrazak Bello-Barkindo ne ya bayyana hakan a wata sanarwa da ya fitar ranar Talata a Abuja.

 

Ya ce ana sa ran batu kan halin da tattalin arziki kasar nan ke ciki zai mamaye kaso mafi yawa na abubuwan da za a tattauna a taron.

 

Barkindo yace ba gaskiya ba ne, rahotannin da wasu kafafen yada labarai a ke yadawa cewa gwamnonin sun bai wa shugaban kasa shawara da ya tilasta wa ma’aikatan gwamnati masu shekaru 50 zuwa sama ritayar dole.

 

A cewarsa, taron zai kasance na farko a wannan Shekarar ta 2022 da gwamnonin za su yi tare a kan tattalin arzikin kasa.

 

Bello-Barkindo ya ce gwamnonin za su kaddamar da asusun kula da lafiya a matakin farko da kuma tsarin bankin duniya SFTAS kafin su shiga taron, wanda ake sa ran za a fara da karfe biyu na rana.

 

A cewarsa gwamnonin za Kuma su sami sabbin bayanai game da shirin farfado da tattalin Arzikin Kasa bayan cutar Covid19

Latest stories

2023 ita ce shekara mafi muni ga yan jarida.

Hukumar Kare Haƙƙin Ɗan'adam ta Majalisar Ɗinkin Duniya ta...

Muna duba batun mafi karancin albashi-Gwamnoni.

Kungiyar gwamnonin kasar nan, ta ce kawo yanzu tuni...

Related stories

2023 ita ce shekara mafi muni ga yan jarida.

Hukumar Kare Haƙƙin Ɗan'adam ta Majalisar Ɗinkin Duniya ta...

Muna duba batun mafi karancin albashi-Gwamnoni.

Kungiyar gwamnonin kasar nan, ta ce kawo yanzu tuni...