Gwamnan Kano Abdullahi Umar Ganduje, ya tura da karin sunan mutum daya da majalisar dokokin Kano zata tantance a matsayin wadanda za a nada kwamishinoni.
Majalisar ta karbi sunan karin mutum dayan Dakta Ali Musa Burum Burum, a yau Talata.
A ranar Litinin data gabata ne gwamna Ganduje ya aikewa da majalisar sunayen mutane takwas da za a tantance tare da amincewa a nada su kwamishinoni a ma’aikatu daban daban.
Hakan ya biyo bayan ajiye aiki da wasu kwamishinonin sukayi don tsayawa takara a matakai daban daban a zaben badi dake tafe.
Ya zuwa yanzu dai mutane tara ake sa ran majalisar dokokin zata tantance a ranar Litinin mai zuwa.