Saurari premier Radio
40.7 C
Kano
Tuesday, April 23, 2024
Saurari Premier Radio
HomeLabaraiGwamnonin Najeriya zasu gudanar da taro kan tattalin arziki.

Gwamnonin Najeriya zasu gudanar da taro kan tattalin arziki.

Date:

Mukhtar Yahya Usman

 

Gwamnonin jihohi kasar nan 36 za su gidanar da wani muhimmn taro a ranar Laraba a Abuja domin tattauna batutuwan da suka shafi tattalin arziki da matsalolin tsaro da sauran kalubalen da ke addabar al’ummar kasar.

 

Daraktan yada labaran gwamnonin kasar nan Abdulrazak Bello-Barkindo ne ya bayyana hakan a wata sanarwa da ya fitar ranar Talata a Abuja.

 

Ya ce ana sa ran batu kan halin da tattalin arziki kasar nan ke ciki zai mamaye kaso mafi yawa na abubuwan da za a tattauna a taron.

 

Barkindo yace ba gaskiya ba ne, rahotannin da wasu kafafen yada labarai a ke yadawa cewa gwamnonin sun bai wa shugaban kasa shawara da ya tilasta wa ma’aikatan gwamnati masu shekaru 50 zuwa sama ritayar dole.

 

A cewarsa, taron zai kasance na farko a wannan Shekarar ta 2022 da gwamnonin za su yi tare a kan tattalin arzikin kasa.

 

Bello-Barkindo ya ce gwamnonin za su kaddamar da asusun kula da lafiya a matakin farko da kuma tsarin bankin duniya SFTAS kafin su shiga taron, wanda ake sa ran za a fara da karfe biyu na rana.

 

A cewarsa gwamnonin za Kuma su sami sabbin bayanai game da shirin farfado da tattalin Arzikin Kasa bayan cutar Covid19

Latest stories

Related stories