Mukhtar Yahya Usman
A ranar Litinin din nan ne dan takarar shugaban Najeriya na jam’iyyar NNPP, Sanata Rabi’u Musa Kwankwaso, zai gabatar da mataimakinsa ga ‘yan kasar.
Wasu hotuna da dan takarar ya wallafa a shafinsa na Facebook sun nuna tsohon gwamnan na Jihar Kano da tawagarsa suna duba babban dakin taro na International Conference Centre da ke Abuja, inda za a gudanar da taron.
A makon jiya ne Sanata Kwankwaso ya Fasto Idahosa, dan asalin Jihar Edo da ke Kudu maso Kudancin Najeriya, a matsayin mutumin da zai yi masa mataimaki a zaben 2023.
Faston, wanda fitaccen mawakin bushara ne, ya taɓa samun lambar yabo ta Majalisar Dinkin Duniya a matsayin jakadan zaman lafiya, saboda gagarumar gudunmawar da ya bayar wajen ci gaban bil adama da zaman lafiya ta hanyar wa’azinsa.
Ya fitar da kundi uku na jerin waƙoƙin bushara a baya.
Bishop Isaac Idahosa shi ne shugaba, kuma babban Fasto na cocin God First Ministry, wadda aka fi sani da Illumination Assembly, da ke Lekki Ajah, a jihar Legas.
Cocin da ya kafa sama da shekaru 25 da suka gabata.