Saurari premier Radio
41.1 C
Kano
Monday, April 29, 2024
Saurari Premier Radio
HomeLabarai2023: Kwankwaso zai kaddamar da Pastor a matsayin mataimakinsa

2023: Kwankwaso zai kaddamar da Pastor a matsayin mataimakinsa

Date:

Mukhtar Yahya Usman
A ranar Litinin din nan ne dan takarar shugaban Najeriya na jam’iyyar NNPP, Sanata Rabi’u Musa Kwankwaso, zai gabatar da mataimakinsa ga ‘yan kasar.

Wasu hotuna da dan takarar ya wallafa a shafinsa na Facebook sun nuna tsohon gwamnan na Jihar Kano da tawagarsa suna duba babban dakin taro na International Conference Centre da ke Abuja, inda za a gudanar da taron.

A makon jiya ne Sanata Kwankwaso ya Fasto Idahosa, dan asalin Jihar Edo da ke Kudu maso Kudancin Najeriya, a matsayin mutumin da zai yi masa mataimaki a zaben 2023.

Faston, wanda fitaccen mawakin bushara ne, ya taɓa samun lambar yabo ta Majalisar Dinkin Duniya a matsayin jakadan zaman lafiya, saboda gagarumar gudunmawar da ya bayar wajen ci gaban bil adama da zaman lafiya ta hanyar wa’azinsa.

Ya fitar da kundi uku na jerin waƙoƙin bushara a baya.

Bishop Isaac Idahosa shi ne shugaba, kuma babban Fasto na cocin God First Ministry, wadda aka fi sani da Illumination Assembly, da ke Lekki Ajah, a jihar Legas.

Cocin da ya kafa sama da shekaru 25 da suka gabata.

Latest stories

Ƙungiyar Hamas ta isa birnin Al-Qahira game da tattaunawa kan tsagaita wuta.

Rahotanni daga kasar Masar, sun ce tawagar jami’an kungiyar...

An kashe ƴan ƙato da gora sama da 23 a Barno da Sakkwato.

Rahotanni daga jihohin Borno da Sakkwato sun ce, an...

Related stories

Ƙungiyar Hamas ta isa birnin Al-Qahira game da tattaunawa kan tsagaita wuta.

Rahotanni daga kasar Masar, sun ce tawagar jami’an kungiyar...

An kashe ƴan ƙato da gora sama da 23 a Barno da Sakkwato.

Rahotanni daga jihohin Borno da Sakkwato sun ce, an...