Rundunar sojin kasar nan ta ceto daya daga cikin ‘yan matan Chikbok.
Rundunar sojin kasar nan a Talatar nan ta gano wata mai suna Mary Ngoshe, daya daga cikin ‘yan matan makarantar sakandire ta Chibok da Boko Haram suka a shekarar 2014.
Rundunar ta gano tane rike da jariri wanda ake zargin nata ne yayin da suke sunturi a yankin Ngoshe na jihar Borno.
Wannan na kunshene cikin wata sanarwa da rundunar sojin kasar nan ta fitar a shafinta na Twitter a safiyar Laraba.
“Rundunar soji ta 26 yayin sunturi a yankin Ngoshe a jihar Borno ta gano wata mai suna Mary Ngoshe wacce daya ce daga cikin ‘yan matan makarantar sakandire ta Chibok ta aka sace a shekarar 2014”, a wallafar Twitter ta rundunar.