Saurari premier Radio
36.9 C
Kano
Friday, May 17, 2024
Saurari Premier Radio
HomeLabaraiZamu hada hannu da hukumar dake kulla da ayyukan majalisa domin cigaban...

Zamu hada hannu da hukumar dake kulla da ayyukan majalisa domin cigaban jihar Kano: Shugaban majalisar dokokin Kano Jibril Isma’il Falgore

Date:

Majalisar dokokin Kano zata hada hannu da hukumar dake kula da ayyukan majalisa wajen yin aiki tare domin cigaban majalisar da jihar Kano baki daya.

Shugaban majalisar Jibril Isma’il Falgore, ne ya bayyana haka yayin da shugabanin hukumar kula da ayyukan majalisar suka kai masa ziyara a ofishin sa a Alhamis din nan.

Ya ce kofa a bude take ga hukumar domin sanar da majalisar bukatun su.

Da yake jawabi shugaban hukumar kula da ayyukan majalisar ta jihar Kano Nasiru Mu’azu Kiru, ya ce sun ziyarci shugaban majalisar ne domin taya su murnar matsayin da suka samu.

Nasiru Mu’azu Kiru, ya ce daga sanda aka kafa hukumar zuwa yanzu ta cimma nasarori da dama musamman na ciyar da ma’aikatan hukumar gaba.

Latest stories

Related stories