Gwamnan jihar Katsina, Malam Dikko Radda, ya goyi bayan da tsayar da Sanata Godswill Akpabio da Barau Jibrin a matsayin wadanda za su shugabantci majalisar dattawa ta 10 ta kasa.
Babban Sakataren Yada Labaran Gwamnan Malam Ibrahim Kaula, ne ya bayyana hakan a wata sanarwa da ya raba wa manema labarai ranar Lahadi a Katsina.
A cewarsa, Radda ya bayyana goyon bayan sa ne a lokacin da Akpabio da Barau suka jagoranci tawagar yan majalisar dattawan kasar suka kai masa ziyarar ban girma a dakin taro na jihar Katsina, a Abuja.
Sanata Akpabio wanda tsohon gwamnan Akwa Ibom ne kuma tsohon ministan harkokin Neja Delta da kuma Sanata Jibrin mai wakiltar mazabar Kano ta tsakiya, su ne jamiyyar APC ta zaba a matsayin shugaban majalisar dattawa da mataimakinsa.