Rundunar yan sandan jihar Kano tace ta tura jamiāai sama da dubu 18 domin sa’ido da kuma tabbatar da an gudanar da zaben kasar nan lafiya.
Kwamishinan yan sandan Kano, CP Mamman Dauda ne ya bayyana hakan a wani taron manema labarai da aka gudanar a shalkwatar rundunar da ke Bompai a Kano.
Yace a kokarinsu na ganin an yi zabe a tsaftace kuma cikin kwanciyar hankali, rundunar ta kama mutane 365 da ake zargi da aikata laifuka daban-daban a Kano cikin makonni bakwai da suka gabata.
Ya kara da cewa a lokuta da dama, rundunar ta kama tare da gurfanar da yan siyasa da laifuka daban-daban.