Ma’aikatar jin ki da kare afkuwar bala’ai ta ce nan ba da dadewa ba za ta biya ma’aikatan rukunin C na shirin Npower hakkokinsu.
Ma’aikatar ta bayyana haka ne a cikin wata sanarwa mai dauke da sa hannun ministar maaikatar, Sadiya Umar Farouk da shafin Npower ya wallafa a kafar Facebook.
Sanarwar ta ce a cikin wannan mako za a biya ma’aikatan na Npower alawus-alawus dinsu na Oktoba, Nuwamba da Disamba, 2022.
A cewar sanarwar, an samu tsaiko wajen biyan alawus-alawus din ne sakamakon wasu matsaloli da suka shafi tangardar na’ura da kuma karkare shekarar kudi ta 2022.
Tun a Oktoba, 2022 ne ma’aikatan Npower na Rukunin CII suka fara ayyuka a wurare daban-daban, amma ba a taba ba su alawus ba.