Karibullah Abdulhamid Namadobi
An sako tsohon mataimakin gwamnan jihar Nassarawa Farfesa Onje Gye-Wado da wasu ‘yan bindiga suka sace ranar 7 ga watan Afrilu.
Jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yan sandan jihar DSP Ramhan Nansel ne ya tabbatar da hakan ga kamfanin dillancin labarai na kasa NAN a yau Litinin.
DSP Ramhan Nansel ya ce tsohon mataimakin gwamnan ya samu iskar yanci ne da misalin karfe 9:00 na daren ranar Lahadi data gabata, kuma ya sake haduwa da iyalansa.
Ya kara da cewa ‘yan sandan ba su da masaniyar wani kudin fansa da aka biya kafin a sako shi.
A cewarsa, an saki shine ne saboda matsin lamba da hadin gwiwar jami’an tsaro suka yi wa masu garkuwa da mutanen.