Kafofin yada labaran Iran sun ce Tehran ta gabatar wa Pakistan sabon daftarinta na tattaunawa da Amurka.
Ba a bayar da wani ƙarin bayani kan abin da daftarin ya ƙunsa ba.
Da safiyar jiya Juma’a ne shugaban hukumar shari’a ta ƙasar Iran ya bayyana cewa, Tehran a shirye take ta tattauna amma ba za ta amince a tursasa mata amicewa da sharuɗɗa ba.
A ranar Talata, shugaban Amurka Donald Trump ya nuna rashin jin daɗinsa kan daftarin da Iran ta gabatar masa a baya.
Ya zuwa yanzu dai ba a sanya wata sabuwar ranar tattaunawa ba, amma rahotanni sun ce an yi wa Donald Trump bayani kan shirye-shiryen yiwuwar kai sabbin hare-haren soji.
