Saurari premier Radio
33.9 C
Kano
Saturday, May 4, 2024
Saurari Premier Radio
HomeLabaraiShugaban daliban Yusuf Maitama Sule ya bukaci a kara adadin sabbin daliban...

Shugaban daliban Yusuf Maitama Sule ya bukaci a kara adadin sabbin daliban da ake wa Gwajin lafiya

Date:

 

Tafida Akilu wanda shine sabon shugaban kungiyar dalibai na jami’ar ta Yusuf Maitama Sule dake nan a jihar kano yayi  kira da a kara adadin sabbin daliban da ake duba lafiyar su a asibitin jamiar dake mazaunin ta na dindin a Kabuga.

 

Tafida yayi wannan kira ne a yayin wani rangadi da yayi a safiyar yau laraba  domin ganin yadda duba lafiyar daliban yake gudana.

 

Wannann duba lafiyar ana yin sa ne ga dukkanin sababbin daliban da aka bawa gurbin karatu a jami’ar, domin tabbatar da cikakkiyar lafiya kafin fara karatu.

 

A yayin ziyarar tasa Tafida ya tattauna da Jami’an hukumar lafiya na jami’ar dake cikin makarantar domin ganin an kara adadin daliban da ake dubawa a rana domin ganin an saukakawa daliban wahalar azumi.

 

A karshe shugaban daliban yayi kira da sabbin daliban da su dena cinkushewa a can sashin na Kabuga da suke zuwa daya sashin dake kofar Nasarawa.

 

 

Latest stories

2023 ita ce shekara mafi muni ga yan jarida.

Hukumar Kare Haƙƙin Ɗan'adam ta Majalisar Ɗinkin Duniya ta...

Related stories

2023 ita ce shekara mafi muni ga yan jarida.

Hukumar Kare Haƙƙin Ɗan'adam ta Majalisar Ɗinkin Duniya ta...