Tafida Akilu wanda shine sabon shugaban kungiyar dalibai na jami’ar ta Yusuf Maitama Sule dake nan a jihar kano yayi kira da a kara adadin sabbin daliban da ake duba lafiyar su a asibitin jamiar dake mazaunin ta na dindin a Kabuga.
Tafida yayi wannan kira ne a yayin wani rangadi da yayi a safiyar yau laraba domin ganin yadda duba lafiyar daliban yake gudana.
Wannann duba lafiyar ana yin sa ne ga dukkanin sababbin daliban da aka bawa gurbin karatu a jami’ar, domin tabbatar da cikakkiyar lafiya kafin fara karatu.
A yayin ziyarar tasa Tafida ya tattauna da Jami’an hukumar lafiya na jami’ar dake cikin makarantar domin ganin an kara adadin daliban da ake dubawa a rana domin ganin an saukakawa daliban wahalar azumi.
A karshe shugaban daliban yayi kira da sabbin daliban da su dena cinkushewa a can sashin na Kabuga da suke zuwa daya sashin dake kofar Nasarawa.