Saurari premier Radio
40.9 C
Kano
Saturday, May 4, 2024
Saurari Premier Radio
HomeLabaraiSakamakon binciken Tukur Mamu zai kada zuciya-DSS

Sakamakon binciken Tukur Mamu zai kada zuciya-DSS

Date:

Mukhtar Yahya Usman

 

Hukumar DSS ta ja kunnen masu yin kalaman rashin ‘kan gado’ game da kama Tukur Mamu mai shiga tsakanin ‘yan ta’adda da gwamnati.

 

Hukumar ta ce sakamakon binciken da take gabatarwa abune mai rikitarwa da zai bada mamaki.

 

Jami’in hulda da jama’a na hukumar Peter Afunanya ne ya bayyana haka a Abuja ranar Lahadi.

 

Ya ce gargadin ya zama dole la’akari da yadda wasu ke yada kalaman batanci ga hukumar tun bayan kama Mamu a shafukansu na sada zumunta.

A cewar hukumar ba za ta rudu da labaran da wasu jaridu da shafukan sada zumunta ke wallafawa ba da zai dauke mata hankali.

Ya ce akwai bukatar a barsu suyi bincike cikin nutsuwa, wanda sakamakonsa abune mai matukar razanarwa.

 

“A halin yanzu, Hukumar za ta daina tsokaci kan batun har zuwa lokacin da kotu za ta yanke hukunci,” in ji shi.

 

Jamian tsaro na Kasa da Kasa ne dai suka kama Tukur Mamu afilin jirgin saman Alkahira na kasar Masar.

Latest stories

2023 ita ce shekara mafi muni ga yan jarida.

Hukumar Kare Haƙƙin Ɗan'adam ta Majalisar Ɗinkin Duniya ta...

Related stories

2023 ita ce shekara mafi muni ga yan jarida.

Hukumar Kare Haƙƙin Ɗan'adam ta Majalisar Ɗinkin Duniya ta...