Saurari premier Radio
38.9 C
Kano
Wednesday, April 24, 2024
Saurari Premier Radio
HomeLabaraiYajin Aikin ASUU: Kotu ta ɗage sauraron ƙarar da gwamnatin tarayya ta...

Yajin Aikin ASUU: Kotu ta ɗage sauraron ƙarar da gwamnatin tarayya ta shigar da ASUU

Date:

Shehu Usman Salihu

 

A zaman farko, kotun masana’antu ta Ƙasa ta ɗage shari’ar da ke tsakanin gwamnatin tarayya da kungiyar malaman jami’o’i, ASUU, zuwa ranar 16 ga watan nan na Satumba da muke ciki.

 

Mai shari’a Polycap Hamman ta ɗage sauraron shari’ar don baiwa ɓangarorin biyu damar shigar da bayanan da su ka dace na ƙarar.

 

Kakakin ma’aikatar kwadago da samar da aikin yi, Olajide Oshundun, ya bayyana cewa ministan kwadago da samar da ayyuka Chris Ngige ne ya miƙa batun ga magatakardar kotunan masana’antu ta kasa, inda ya ƙara da cewa daga nan ne gwamnati ta garzaya kotun.

 

Ya kara da cewa ma’aikatar ta roƙi kotun da ta baiwa ASUU umarnin janye yajin aiki, yayin da ake kokarin shawo kan rikicin.

 

Idan za’a iya tunawa ASUU ta tsunduma yajin aikin ne tun a watan Fabrairun shkarar nan ta 2022, wanda ya kai ga rufe jami’o’in gwamnati na tsawon watanni takwas zuwa yanzu.

Latest stories

Hukumar EFCC ta musalta zargin da ake mata na fara bincikar tsohon Gwamnan kogi.

Shugaban hukumar EFCC mai hukunta masu yiwa tattalin arziki...

Majalisar dokokin Kano ta nemi a dakatar da KEDCO kan yanke wuta.

Majalisar Dokokin jihar Kano ta bukaci gwamnatin jihar data...

Related stories

Hukumar EFCC ta musalta zargin da ake mata na fara bincikar tsohon Gwamnan kogi.

Shugaban hukumar EFCC mai hukunta masu yiwa tattalin arziki...

Majalisar dokokin Kano ta nemi a dakatar da KEDCO kan yanke wuta.

Majalisar Dokokin jihar Kano ta bukaci gwamnatin jihar data...