Mataimakin Shugaban Najeriya, Kashim Shettima ya tashi daga Abuja zuwa birnin Dallas na kasar Amurka, domin wakiltar shugaba Bola Tinubu a taron kasuwanci na Amurka da Afirka na 2024 wanda kungiyar kamfanoni kan Afirka ta shirya.
A wata sanarwa da babban mai taimaka nasa na musamman kan harkokin yada labarai Stanley Nkwocha ya fitar, ya ce mataimakin shugaban kasar zai bi sahun sauran shugabannin siyasa da na kasuwanci a fadin Afirka a wajen taron da ke kunshe da manyan batutuwan da za a tattauna da harkokin kasuwanci da kulla kawance a fannonin cinikayya.
Daga cikin shugabannin Afirka da ake sa ran za su halarci taron akwai Shugaba Joseph Boakai na na kasar Liberia; Shugaban kasar Malawi Lazarus Chakwera; Shugaba Joao Lourenco na Jamhuriyar Angola; Shugaba Mokgweetsi E. K. Masisi na Jamhuriyar Botswana; Shugaba José Maria Neves na Jamhuriyar Cabo Verde,
Baya ga taron kolin, ana sa ran Shettima zai yi jawabi a wani taro da zai duba batun zuba jari a fannonin ababen more rayuwa a nahiyar Afirka tare da mai da hankali kan tasiri da samun riba.