Tsohon gwamna Kano Abdullahi Umar Ganduje ya gargadi gwamnatin Kano da ta maida hankali wajen sauke nauyin da ke kanta maimakon kokarin bata masa suna.
Ganduje na wannan bayani ne cikin wata sanarwa da jama’in yada labaran sa Edwin Elufu ya fitar a Juma’a a matsayin martini kan zargin a akai masa.
A ranar Alhamis ne gwamnatin Abba Kabir Yusif ta zargi Ganduje da matarsa Hafsat da wasu mutum Uku kan zargin cin hancin kudi Dala dubu 413 da kuma sama da naira biliyan
A cewar Ganduje yunkurin abin takaici ne, kuma zai dauke hankalin al’ummar jihar Kano ganin cewa babu wani abu a kasa da gwamantin zata iya nunawa, duk kuwa da makudan kudin da take karba daga gwamnatin tarayya.
Ya kara da cewa kokarin gurfanar dashi ya saba da umarnin wata babbar kotu a Kano da tace gwamnatin tarayya ce kadai ke da hurumin gurfanar da shi gaban kotu.