kotu ta baiwa gwamnatin jihar Kano wa’adin mako daya ta biya diyyar Naira miliyan dubu 30 ga yan kasuwar da aka rushewa shaguna a babban masallacin idi na Kano.
Kwanaki 34 ke nan tun bayan da babbar kotun jiha a nan kano, taci tarar gwamnatin kano Naira Biliyan 30 diyyar rusau din da akayi a filin masallacin idi dake kofar mata a jihar nan.
Gwamnatin ta kano takalubalanci Hukuncin a babbar kotun daukaka kara inda ta nemi a dakatar da hukuncin, sai dai kotun tace biyan wadancan kudaden sun zama dole in har gwamnatin na neman a dakatar da hukuncin kafin kammala shari`ar