Kamfanin mai na kasa ya ce shirye shirye tuni sun kammala domin baiwa matatar mai ta dangote gangar danyen mai miliyan 6, a wani mataki na karfafa bangaren ta ce man a cikin gida, maimakon kai shi zuwa kasar waje da nufi a ta ce.
Wani rahoto na musamman da jaridar Punch ta gudanar ya bayyana cewa, karancin danyen mai da matatar ke fuskanta, ya taka rawa wajen koma bayan matatar a ayyukanta, lamarin da ake ganin hakan tamkar abin kunya ne.
To sai dai a wani mataki mai kama da martani kan wannan batu, kamfanin man y ace zuwa nan da watan disamba wato karshen shekarar nan, zai fara baiwa matatar danyen mai ganga milyan 6.
Wani kusa a kamfanin da ya bukaci a asakaya sunasa, ya shaidawa manema labarai cewa, wannan bayar da danyen man ga matatar wani bangare ne na yarjejeniyar kasuwanci da aka cimma tsakanin matatar da kuma kamfanin kwanakin baya a Abuja.