Tsohon shugaban najeriya janar Yakubu Gawon ya karyata labarin dake yawo cewa Allah yayi masa rasuwa.
A wata hira da jaridar vanguard a daren jiya, tsohon shugaban yace yayi mamakin inda aka samo labarin, inda yace yana nan a raye kuma cikin koshin lafiya.
A yammacin jiya litinin ne dai labarin rasuwar sa ya karade shafukan sada zumunta, Janar Gowon dai ya shugabanci kasar nan daga shekarar 1966 zuwa 1975 bayan hambarar da gwamnatin manjo janar Aguiyi Ironsi
An dai haifeshi ne a ranar 19 ga watan oktoba 1934, yanzu haka yana da shekaru 89 a duniya.