Shugaban hukumar EFCC mai hukunta masu yiwa tattalin arziki zagon kasa, Ola Olukayide, ya musanta zargin shi ne ya fara bincikar tsohon gwamnan Kogi, Yahya Bello.
A wata hira da manema labarai jiya a Abuja, shugaban na EFCC ya ce shi ma gadar binciken ya yi daga tsohon shugaban hukumar.
Ya kuma ce ba shi da wani dalilin yi wa Yahya Bello bi-ta-da-kulli, illa kishin ganin an samu ci gaba a kasar nan, musamman ganin yadda cikin wata shida da fara aiki a hukumar, aka samu damar kwato kudi naira milyan dubu 120 daga hannun ‘yan damfara.
Mr Olukayide, ya musanta cewa jami’ansu na aiki da son zuciya tun bayan da ya kama aiki a bara, kuma matukar ba su bibiyi shari’ar Yahya Bello ba, EFCC ba za ta iya bincikar kowa ba ke nan.