Ministan sifuri na kasar nan Mu’azu Sambo ya ce Gwamnatin kasar nan ta shirya tsaf domin dawo da zirga zirgar jirgin kasan Kaduna Abuja a wannan watan na nuwamban da muke ciki.
An dakatar da aikin jirgin kasan tun bayan wani harin bom da yan bindiga suka kai tare da sace wasu daga cikin fasinjojin jirgin a ranar 28 ga watan Maris din da ya gabata.
A kwanakin baya ministan yayi alkwari cewa baza’a dawo da aikin jirgin har se an sako fasinjojin da aka sace gaba daya.
Da yake sanar da dawowar ministan ya bayyana cewa an tsaurara matakan tsaro a hanyar domin kaucewa faruwar irin wannan lamarin.
Ya kuma kara da cewa sun koyi darasi daga harin da aka kai inda ya bayyana cewa zasuyi kokarin ganin hakan bai kara faruwa ba.