Babban bankin kasa CBN, ya amince da kara wa’adin kwana 10 domin ci gaba da sauyin tsafin kudaden 200, 500 da Kuma 1000 a fadin kasar nan.
Premium Times ta rawaito cewa
Wannan na zuwa ne bayan da Gwamna bankin kasa Godwin Emefiele, ya sanar da hakan a wannan Lahadin.
Yanzu haka dai za a ci gaba da sauyin tsafin kudaden zuwa ranar 10 ga Fabrairu mai kamawa.
A baya dai CBN ya bayyana ranar Talata 31 ga Janairun da muke ciki a matsayin ranar da wa’adin zai ci cika.