Bankin kasa na CBN dai ya ayyana ranar 31 ga watan Janairun da muke ciki, shi ne karshen wa’adin amfani da tsaffin kudi a fadin kasar nan zai kare.
To Amma a gefe guda an jiyo Majalisar Wakilai tace akwai yiwuwar kara wa’adin idan har Gwamnan Bankin CBN Godwin Emefele ya halarci zaman da za suyi dashi ranar Talata mai zuwa .
Sai dai kuma ana kallon har kawo yanzu miliyoyin Yan Najeriya ba su kashe sabbin kudi ba.
A gabar da Kuma wasu ke kallon sabbin kudin basu wada ta a hannun mutane ba.
Koda yake dama CBN yace manufar shine takaita zurga zurgar kudade a hannun jama’a.