Firaministan Isra’ila Benjamin Netanyahu ya nanata kudirin sojojin Isra’ila na kai farmaki ta kasa a Rafah, ko da anyi sulhu da Hamas, ko akasin haka.
Ya ce, sojojin Isra’ila za su shiga Rafah domin kawar da ayarin dakarun Hamas.
Sanarwar da ofishin Firaministan ya fitar, ta ce tilas ne a kwato dukkan Yahudawan da suka rage a hannun Hamas, wadanda ta yi garkuwa da su ranar 7 ga watan Oktobar bara.
Wani babban jami’in Isra’ila da ya nemi a sakaya sunansa, ya shaidawa manema labarai cewa, gwamnati za ta jira har zuwa daren yau Laraba domin jin matakin da Hamas za ta dauka game da batun tsagaita wuta.
Ya kara da cewa, Isra’ila za ta yanke shawara da zarar Hamas ta bayyana matsayinta dangane da shawarwarin da aka cimma a tattaunawar tsagaita wuta da aka gudanar a birnin Al’Qahirar kasar Masar.