Gwamnan jihar Borno ya rufe gidan radiyon Al-ansar mai zaman kansa a jihar Borno.
Wannan na zuwa ne jim kadan bayan da kungiyar kafafe shugabanin kafafen yada labarai suka kai masa ziyar taya murna a yau Laraba.
Muhammad Bukar Wani dan jarida a jihar Borno ya shaidawa Premier Radio cewa bayan gaisawa da shugabannin ne gwamanan ya dauki zafi.
A cewarsa gwamnan ya zargi gidan radiyon da baiwa yan adawa damar fadin albarkacin bakinsu lokacin da ake tsaka da siyasa.
Hakan ce ma ta Sanya ya bayar da umarnin rufe gidan radiyon bisa fakewa da ba a biya haraji ba.
Munyi kokarin jin ta bakin mahukuntan jihar ta Borno amma hakanmu bai cimma ruwa ba.